Kotun ta yanke hukunci ga wanda ya chakawa jami’in NDLEA wuka a Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Wata kotun tarayya dake zaman a Kano karkashin jagorancin mai Shari’a MN Yunusa ta yanke hukunci ga wasu mutane 22 da aka same su da laifin tu’ammali da miyagun kwayoyi, daga Cikin su kuma akwai wanda ya tsakawa jami’in hukumar NDLEA wuka.

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kano ce ta samu nasarar kama mutane 22 a cikin watan Yulin 2024 a yakin da take yi da safarar miyagun kwayoyi da kuma sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar reshen jihar kano Sadiq Muhammad Maigatari ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aikowa kadaura24 a Kano.

Talla
Talla

Ya ce daga cikin wadanda aka yankewa hukuncin har da Abubakar Muazu, wanda aka kama shi da caka wa wani jami’in NDLEA da kansa Mu’azu wuka. Jami’an sun kama Muazu Sannan suka kama yaransa da kuma kwato wasu kwayoyi da yake sayarwa .

Bayan samun sa da laifi Kotun ta yankewa Abubakar Muazu hukuncin daurin shekaru 3 a gidan yari daga hannun . “Wannan laifin zai zama izina ga duk masu neman kawo cikas ga hukumar NDLEA wajen gudanar da muhimmin aikinta”.

Sojoji Sun Gargaɗi Masu Shirin Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

Sanarwar ta ce hukumar ba zata yi kasa a gwiwa ba wajen cigaba da yakar masu sha da fataucin miyagun kwayoyi a jihar kano da kasa baki daya.

Yayin da yake godiya ga al’umma shugaban hukumar NDLEA, Brig. Janar Mohammed Buba Marwa, ya bukaci al’umma da su cigaba da baiwa jami’an hukumar hadin kai da goyon baya don cimma manufarsu.

Sanarwar ta ce Kwamandan NDLEA na jihar Kano, CN Abubakar Idris Ahmad ya yi gargadi ga masu safarar miyagun kwayoyi a Kano cewa, duk wata barazana ko tashin hankali ba zai hana jami’an hukumar bibiyar tare da gurfanar da su a gaban Shari’a ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...