Yanzu-yanzu: Tinubu ya na ganawa da gwamnoni kan batun zanga-zangar tsadar rayuwa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

A halin yanzu dai shugaban ƙasa Bola Tinubu, yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC da wasu a a fadar shugaban kasa da ke birnin Abuja.

Duk da cewa ba a bayyana dalilin taron ga manema labarai ba wanda suke gudanar da shi yau Alhamis, a fadar gwamnati amma ana kyautata zaton yana da nasaba da shirin zanga-zangar tsadar rayuwa da aka shirya gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta, 2024.

Talla
Talla

Shugaban kungiyar gwamnonin kuma gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma ne, ya jagoranci tawagar gwamnonin zuwa fadar shugaban kasa tare da shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF), kuma Gwamna jihar Kwara, AbdulRazaq AbdulRahman.

Kotun ta yanke hukunci ga wanda ya tsakawa jami’in NDLEA wuka a Kano

Haka kuma an ga mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shuaibu, da Gwamnan jihar Benue, Hycinth Alia da takwarorinsa Uba Sani na jihar Kaduna da na jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, da dai sauransu duk a fadar shugaban ƙasa.

Talla

Sauran wadanda suka halarci taron sun hadar da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribado da Ministan Kudi Wale Edun da Atiku Bagudu ministan kasafi da tsare-tsare da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...