Yanzu-yanzu: Tinubu ya na ganawa da gwamnoni kan batun zanga-zangar tsadar rayuwa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

A halin yanzu dai shugaban ƙasa Bola Tinubu, yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC da wasu a a fadar shugaban kasa da ke birnin Abuja.

Duk da cewa ba a bayyana dalilin taron ga manema labarai ba wanda suke gudanar da shi yau Alhamis, a fadar gwamnati amma ana kyautata zaton yana da nasaba da shirin zanga-zangar tsadar rayuwa da aka shirya gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta, 2024.

Talla
Talla

Shugaban kungiyar gwamnonin kuma gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma ne, ya jagoranci tawagar gwamnonin zuwa fadar shugaban kasa tare da shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF), kuma Gwamna jihar Kwara, AbdulRazaq AbdulRahman.

Kotun ta yanke hukunci ga wanda ya tsakawa jami’in NDLEA wuka a Kano

Haka kuma an ga mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shuaibu, da Gwamnan jihar Benue, Hycinth Alia da takwarorinsa Uba Sani na jihar Kaduna da na jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, da dai sauransu duk a fadar shugaban ƙasa.

Talla

Sauran wadanda suka halarci taron sun hadar da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribado da Ministan Kudi Wale Edun da Atiku Bagudu ministan kasafi da tsare-tsare da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...