Ni Dan Siyasa Ne Ba Dan Kungiya ba – Sanata Kawu Sumaila

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Sanatan Kano ta kudu a zauren majalisar Dattawan Nigeria, Sulaiman Abdurrahman Kawu Sumaila ya ce shi ba dan wata Kungiya ba ne, kawai abun da ya sani shi dan siyasa ne.

” Yau Shekaru 33 ban taba cire kafa ta daga harkar siyasa ba, don haka idan anyi min adawa bata damuna, domin nima na taba zama a matsayin dan adawa”.

Kadaura24 ta rawaito Kawu Sumaila ya bayyana hakan cikin yayin da yake martani ga masu ganin baikensa saboda ya gabatar da kudirin.

Talla

“Ita Kwankwasiyya kungiya ce a cikin siyasa kuma nima Ina da kungiyar waraka, kungiyar da bana cikin ita ce irin kungiyar cigaban gari ko cigaban jiha ko kuma ci gaban wani to duk bana wannan kawai dan siyasa ne ni”. Kawu Sumaila

Sanata Kawu Sumaila ya gabatar da kudirin kirkirar sabuwar jiha daga Kano

Ya ce jagoran Kwankwasiyya ya san abun da mutanen kano ta kudu suke so shi yasa lokacin zabe ya bashi goyon baya saboda yasan cewa al’ummar kano ta kadu shi suke so shi yasa kuma suka zabe shi.

Rusau: Gwamnatin Kano Ta Bayyana Matsayarta Kan Gine-Ginen Dake Hanyar BUK

An tambaye shi cewa, shin wannan kalaman nasa an ya basa nufin fito-na-fito da tsarin Kwankwasiyya ? , kawu Sumaila ya ce Sam ba haka ba ne.

A cikin hira da Manema labarai Kawu Sumaila ya ce ya gabatar da kudirin kirkirar sabuwar jiha ta Tiga ne don cigaban al’ummar da yake wakilta kuma ba ya nadamar abun da yayi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Cire Maryam Sanda Daga Jerin Wadanda Za a Yi Wa Afuwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bada umarnin a...

Majalisar Kano ta buƙaci a soke ɗaukar aikin kwastam da aka yi a kwanan nan

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga dukkan...

‎ ‎Kuskure ne Tinubu ya cigaba da ciyo wa Nigeria bashi bayan ya cire tallafin mai – Sarki Sanusi

‎ ‎ ‎Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN),...

Shugaban Karamar Hukumar Ungogo Ya Raba Kwamfutoci Ga Daliban da Suka Samu Tallafin Karatu Zuwa Kasar Indiya

Shugaban Karamar Hukumar Ungogo, Hon. Tijjani Amiru Bilyaminu Rangaza,...