Shugaba Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro

Date:

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika wa Majalisar Dattawan Nigeria da buƙatar tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro da ya naɗa kwanan nan.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya karanta wasiƙar shugaban ƙasa yayin zaman majalisar na ranar Talata.

FB IMG 1753738820016
Talla

A cikin jerin sabbin hafsoshin, Tinubu ya naɗa Manjo Janar Olufemi Oluyede a matsayin Babban Hafsan Tsaro, Manjo Janar Waheedi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Rear Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Rundunar Sojan Ruwa, Air Vice Marshal Kennedy Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama, da kuma Manjo Janar Emmanuel Undiendeye a matsayin Daraktan Tsaron Sirri na Ƙasa.

INEC ta ce ta kammala shirye-shiryen zaben gwamna na Anambra

A cikin wasiƙarsa, Shugaba Tinubu ya roƙi majalisar da ta hanzarta tabbatar da waɗannan naɗe-naɗe, domin a cewarsa, hakan zai taimaka wajen inganta gyaran tsaro da gwamnatinsa ke aiwatarwa tare da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanci, ‘yan bindiga da sauran barazanar tsaro.

Majalisar ta tura buƙatar shugaban ƙasa zuwa wani kwamiti domin gudanar da tantancewa da tabbatarwa, wanda za a gudanar a ranar Laraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...