Yadda DSS su ka kashe tare da kama wadanda suka sace mahaifiyar Rarara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS sun kashe daya daga cikin wadanda suka yi garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawakin Hausa, Dauda Kahutu Rarara, yayin da aka ce an kama guda bayan an harbe shi da bindiga.

Majiyar DSS a Kano ta ce jami’an sun kai farmakin ne maboyar masu garkuwa da mutane a cikin dajin Makarfi da ke jihar Kaduna, da sanyin safiyar Juma’a, inda suka yi musu ba-zata a lokacin da suke raba kudin fansa da suka karba.

A cewar majiyar: “Jami’an sun yi nasarar fatattakar masu garkuwar, inda nan take suka kashe daya sannan suka kama wani da ke karbar magani sakamakon harbinsa da bindiga da aka yi, yayin da aka kwato Naira miliyan 26.5 da aka biya su a matsayin kudin fansar mahaifiyar mawakin.”

Talla

Ya ce an kai harin ne bayan da aka samu bayanan sirri cewa masu garkuwar suna dajin Makarfi.

Gwamnan kano ya bayyana dalilinsa na kin dawo da Sarkin Bichi

Ya ce: “aikin ya yi nasara sosai har dayan mai garkuwa da mutane da ke karbar magani yana taimaka wa jami’an da wasu sahihin bayanai kan yadda suka yi garkuwa da ‘yan Najeriya da ba su ji ba ba su gani ba.”

Ya kara da cewa: “A gaskiya ba zan iya tabbatar muku cewa masu garkuwa da mutane Hamisu da Bature Fulani ne ba. Amma dai wanda ke karbar magani, Bature, yana taimaka wa jami’an da bayanan ayyukansu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya bijiro da harajin da zai sa farashin man fetur ya karu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙaddamar...

Sabbin Nau’o’in cutar Shan Inna 4 sun bulla a Kano

Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta jihar...

NDLEA ‘Yan Sanda da Gwamnatin Kebbi Sun Karyata Jita-jitar Samar da Filin Jirgin Sama na Boye a jihar

  Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta...

Kotu a Kano ta kawo karshen Shari’ar wata Tunkiya

Daga Dantala Uba Nuhu, Kura An kawo ƙarshen shari’ar wata...