Gwamnan kano ya bayyana dalilinsa na kin dawo da Sarkin Bichi

Date:

Daga Samira Ahmad

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce girma da darajar Bichi a masarautar kano ta sa tasa bai dawo da Sarkin Bichi ba.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a Kwanakin baya gwamnatin jihar kano ta rushe sabbin masarautu da Ganduje ya samar a shekara ta 2019, bayan rushe dokar masarautun da majalisar dokokin jihar kano ta yi.

” Ita Bichi tana da muhimmanci sosai ga masarautar kano , saboda muhimmancinta ba konne mutum ake kaiwa ya zama hakimi ba, dole sai dan sarki don haka ba mu dawo da ita ba muka bar ta yadda tarihi ya nuna”.

Talla

Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne yayin wani taro na masu ruwa da tsakin jam’iyyar NNPP na kano a gidan gwamnatin jihar.

Ba haka mu ka tsammata daga gareku ba – Atiku Abubakar ga majalisar wakilai

Ya a baya dan sarkin kano shi ake nadawa a matsayin hakimin Bichi hakan tasa bayan rusa masarautun suka bar da a matsayin da take da shi tun asali.

Yayi fatan Sarki Sanusi II zai tura mutum mai kima da zai rike kasar Bichin a matsayin hakimi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...