Kofa ya shirya taron addu’o’i da gangamin motsa Jam’iyyar NNPP

Date:

Daga Zakaria Adam Jigirya

 

Ɗan Majalisa mai wakiltar mazaɓar kananan hukumomin Kiru/Bebeji a jihar Kano, Hon Abdulmumin Jibrin Kofa, a ranar Lahadi ya shirya taron addu’a na musamman a gidansa da ke Kofa, Bebeji, inda ɗaruruwan malamai suka yi wa mazabarsa da Kano da ma Najeriya addu’a.

Daga bisani kuma ɗan majalisar ya shirya babban taron motsa jam’iyya wanda dubban magoya baya suka halarta, inda ya jinjina musu kan jajircewarsu da goyon bayan da suke bayarwa.

Talla

Hon. Kofa ya ba su tabbacin cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ci gaba da bayar da tallafin da kuma ayyukan raya ƙasa da yake yi daga yi daga aljihunsa da kuma na gwamnatin tarayya .

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa tsohon Sanatan Kano ta tsakiya mukami

Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano, Hashimu Sulaiman Dungurawa da ’Yan Majalisar jiha na mazabar Kiru (Abubakar Tasi’u Rabula) da na Babeji (Ali Mohammed Tiga), Shugaban Ma’aikatan Jihar Kano, Abdullahi Musa da kuma dattawa (Alhaji Jibrin Dan-Ako da Alhaji Dankaka Hussaini Bebeji) da

Sani Ibrahim Paki
Hadimin ɗan majalisar kan yaɗa labarai
14-07-2024

Ga hotunan yadda aka gudanar da taron:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...