Yau Katun Ƙoli Za ta Yanke Hukunci Kan Shari’ar Da Tinubu Ya Kai Karar Gwamnonin Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

A yau ne ake sa ran kotun koli za ta yanke hukunci kan karar da gwamnatin tarayya ta shigar a kan gwamnonin jihohi 36, Inda ta ke neman kotun ta tilastawa gwamnonin baiwa kananan hukumomi 774 na kasar nan yancin cin gashin kansu.

Kotun kolin ta sanar da dukkan bangarorin da ke kara ta hannun lauyoyinsu cewa a yau zata yanke hukuncin .

Talla

Kotun kolin dai a ranar 13 ga watan Yuni ta dage yanke hukunci kan karar da ake zargin gwamnatocin jihohi. A zaman da aka yi na karshe, tawagar alƙalai bakwai karkashin jagorancin Mai Shari’a Garba Lawal, ya bayyana cewa a shirye suke da za su yanke hukunci bayan sauraron bahasi daga gwamnonin jihohin kasar nan 36, wadanda manyan lauyoyinsu suka wakilce su.

Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Jihohin dai sun yi zargin cewa Lateef Fagbemi, babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a ba shi da hurumin fara daukar matakin a madadin gwamnatin tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...