NDLEA Za Ta Sanya Kyamara A Jikin Jami’anta

Date:

Hukumar yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi (NDLEA) za ta fara sanya kyamarori a jikin jami’anta domin inganta aikinsu.

Shugaban hukumar, Mohamed Buba Marwa, ya bayyana haka ne a wani taro a Abuja inda aka yi wa wasu jami’ai karin girma a ranar Laraba.

Talla

Marwa ya ce, “Za mu sa kyamarori a jikin jami’anmu a lokacin gudanar da muhimman ayyuka don tabbatar da amincinsu da kuma ingancin ayyukan.”

Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Don kara inganta aikin hukumar, Marwa ya bayyana cewa NDLEA na kafa rassa biyar a Legas da Abuja.

Hukumar ta kara wa jami’anta 5,042 girma, ciki har da manyan hafsoshi biyu zuwa mukamin mataimakin kwamanda-janar.

Marwa ya ce karin girma ya biyo bayan tsauraran gwaje-gwaje da aka yi wa jami’an, yana mai bayar da tabbacin inganta yanayin aikin jami’an hukumar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Za a kashe Naira Miliyan 87 wajen Sanya Interlock a sakatariyar K/H Dala – Surajo Imam

Daga Sani Idris Maiwaya   Gwamnatin jihar Kano ta Amince da...

Yansanda sun Haramta Hawan Sallah a Kano

Daga Abdulmajid Habib   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta haramta...

Sanata Barau ya kai ziyarar jaje ga iyalan ‘yan wasan da suka rasu, ya bayar da gudunmuwar N22m

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I Jibrin, a...

Hawan sallah : Sarki Sanusi ya umarci hakimai su shigo cikin birnin Kano

Majalisar Masarautar Kano ta fitar da wata takarda mai...