Kotun Koli Ta Haramta Wa Gwamnoni Taba Kudaden Kananan Hukumomi

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Kotun Koli ta Najeriya ta haramta wa gwamnoni rikewa da kuma gudanar da kudaden kananan hukumomin jihohinsu.

Mai Shari’a Emmanuel Agim na Kotun Koli ya kuma ba da umarnin tura wa kananan hukumomi kudadensu kai-tsaye daga asusun Gwamnatin Tarayya.

Talla

Ya bayyana cewa ce rike kudaden kananan hukumomi da aka tura daga asusun tarayya da gwamnatocin jihohi suke yi ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya.

Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Da yake sanar da hukuncin a ranar Alhamis, Mai Shari’a Emmanuel Agim, ya ba da umarnin damka wa kananan hukumomi 774 da ke fadin kasar kudadensu don su ci gaba da gudanarwa.

Alkalin ya kuma kori buƙatar da gwamnatocin jihohi suka shigar na kalubantar neman hana su tasarrufi da kudaden kananan hukumomin.

Ya bayyana cewa a tsawon lokacin da jihohi suka ki ba wa kananan hukumomi ’yancin tafiyar da kudaden, gwamnatocin jihohin ne ke yin gaban kansu da kudaden.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...