Gwamnan Kano zai hada kai da Kasar Netherland don inganta noma da sauyin Yanayi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bukaci kasar ta Netherland ta baiwa jihar goyon bayan diflomasiyya domin habaka harkokin noma da rage tasirin sauyin yanayi .

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana ƙudirinsa na kulla huldar diflomasiyya da gwamnatin Holland a ranar Talata lokacin da ya karbi bakuncin Ms Eva De Wit, babbar jami’an a Ofishin Jakadancin Masarautar Netherland dake Najeriya.

A wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin-Tofa, mai magana da yawun gwamnan ya aikowa kadaura24, ta ce gwamna Yusuf ya jaddada tasirin da masarautar ta samu kan noma da sauyin yanayi a Nahiyar Turai.

Hasashen yanayin da zai kasance yau laraba a birnin Kano da wasu jihohin Nigeria

A cewar sanarwar, Gwamna Yusuf wanda ya nuna sha’awarsa bisa yadda kasar Netherland take gudanar da harkokin noma, ya bayyana aniyar gwamnatinsa na samar da hadin gwiwar don inganta harkokin noma a Kano.

Yusuf ya yi amfani da damar ziyarar ta diflomasiyya wajen bayyana wasu aiyuka da gwamnatinsa ta gudanar bunkasa rayuwar matasa da samar da wadataccen Abinchi a jihar Kano.

Hajjin Bana: Ƙasar Saudiyya Ta Samar Da Wata Lema Ta Musamman Ga Mahajjata

Yayin da yake sanar da tawagar kasar Bakin nasa kokarin da gwamnatin sa ta yi na yakar shan muggan kwayoyi a jihar, Gwamna Yusuf ya ce ya bada umarnin bude cibiyoyin koyar da sana’o’i 24 domin karfafawa matasa gwiwa.

A nata bangaren, Ms De Wit wadda ta samu rakiyar Shugaban Ofishin Jakadancin, Hukumar Kula da Hijira ta Duniya, Mista Laurent De Boeck, ta yi alkawarin hada kai da gwamnatin jihar Kano a fannonin inganta rayuwar matasa, samar da abinci da sauyin yanayi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...