Abun da ya faru a majalisar dokokin jihar kano kan batun gyaran dokar masarautu

Date:

Daga Isah Ahmad Getso

 

Kudurin gyaran dokar masarautun jihar Kano ya samu tsallake karatu na daya a zaman majalisar dokokin jiha a yau Laraba.

Kudurin, ya samu kaiwa wannan mataki ne bayan da Akawun majalisar Alhaji Bashir Idris Diso ya gabatar da karatun Kudurin yayin zaman majalisar.

Hasashen yanayin da zai kasance yau laraba a birnin Kano da wasu jihohin Nigeria

Yanzu dai saura karatu na biyu da na uku, idan kudirin ya tsallake waɗannan matakai to majalisar zata gudanar da gyare-gyare akan dokar, kamar yadda yake a tsarin majalisar.

Yau dai rahotanni sun tabbatar da cewar tun da sanyin safiyar wannan rana ta laraba ne aka jibge tarin jami’an tsaro a harabar majalisar dokokin ta jihar kano domin shirin ko ta kwana.

Hajjin Bana: Ƙasar Saudiyya Ta Samar Da Wata Lema Ta Musamman Ga Mahajjata

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a jiya Talata ne dai shugaban masu rinjaye na zauren majalisar ya gabatar da kudurin gaggawa a majalisar domin neman kirawo dokokin masarautun Kano ta shekarar 2019 da kuma ta 2023 domin yi musu gyara.

A Kwanakin baya ne dai kungiyoyi daban-daban suka Rika kira ga majalisar data sake duba Dokar, a gefe guda kuma wasu kungiyoyin na kira ga majalisar da ta yi watsi da bukatar sake duba dokar masarautun ta jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...