Muhimmiyar Sanarwa Daga Rundunar Yan Sandan Jihar Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano tana sanar da daukacin al’umma cewa jami’an rundunar ‘yan sanda mai lamba 52 (PMF) Squadron dake Challawa Kano za su gudanar da atasayen harbi na kwanaki biyu a Hawan Kalibawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano. daga karfe 6 safe zuwa 6 na yamma kullum a Asabar, 11th da Lahadi 12th ga watan Mayu 2024.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda jama’a na rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Iftila’i: Jarumar Fim din Labarina ta yi hatsari tare da mijinta

Sanarwar ta shawarci jama’a musamman mazauna kauyukan Dambazau, Gangaren Dutse, Tumfafi, Kakurum da Dandalama a kananan hukumomin Dawakin Tofa da Ungogo da kewaye da su nisanta daga wajen, kuma kada su firgita da karar harbe-harben atasayen da zasu gudanar.

Kwamishinan ‘yan sanda CP Mohammed Usaini Gumel, FIPMA, psc, ya yabawa al’ummar jihar Kano bisa fahimtar juna, addu’o’i, goyon baya da hadin kai da suke baiwa rundunar a koda yaushe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...