Kotu ta sanya ranar fara sauraron Shari’ar Ganduje kan korar shi daga APC

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Wata babbar kotun jihar Kano ta sanya ranar 27 ga watan Mayu, 2024, domin fara sauraron kararraki guda uku kan dambarwar dakatar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

 

Mai shari’a Usman Malam Na’abba ne ya jagoranci zaman kotun bayan sauraron lauyoyin ɓangarorin biyu, sun sanya ranar da za a ci gaba da sauraren karar.

Da dumi-dumi: NNPC ya sanar da ranar da Zai kawo karshen ƙarancin man fetur a Nigeria

Masu shigar da karar, sun haɗa da: Haladu Gwanjo da Laminu Sani Barguma ta hannun lauyansu, Ibrahim Abdullahi Sa’ad sun shigar da kara mai lamba 13 a ranar 16 ga Afrilu wanda mai bukata na biyu ya goyi bayansu.

Sojoji sun tarwatsa maɓoyar ƴanbindiga, sun kuɓutar da mutane a Taraba

Bayan sauraren bukatun masu shigar da karar tare da yin tambayoyi wanda aka ƙi yarda a amsa a farko, bukatun masu karar na haɗin gwiwa ne da ƙalubalantar hurumin kotun na sauraron karar .

Wanda suka shigar da karar na neman kotu ta yanke hukuncin dakatar da Abdullahi Umar Ganduje na wucin gadi.

Yanzu dai alƙalin kotun ya sanya ranar 27 ga watan mayu na wannan shekarar domin fara sauraren Shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...