Unguwar Hotoro ta sami ci gaba sosai bayan samar da Jami’ar Maryam Abacha – Wani Dillali

Date:

Daga Aminu Yahaya Tudun wada

 

Dillalan filaye a Hotoro da ke birnin Kano sun danganta tashin farashin fili a yankin da samuwar Jami’ar Maryam Abacha da ke Kwanar Maggi a yanki.

Daya daga cikin dillalan filayen, Muhammad Najume ne ya bayyana hakan a yayin wata ganawa da yayi da Kadaura24. Inda ya ce tashin farashin ya fara ne bayan da jami’ar ta fara aiki .

Malam Muhammad ya bayyana cewa filin da ake sayar da shi kan Naira miliyan 20 a shekarar 2023 a yanzu ana sayar da shi a kan Naira miliyan 150 ko sama da haka.

Wannan za a iya danganta shi da yanayin tattalin arziki da kuma samuwar jami’ar a yankin.

Da dumi-dumi: NNPC ya sanar da ranar da Zai kawo karshen ƙarancin man fetur a Nigeria

Jami’ar Maryam Abacha Ta Kawo Cigaba Mai Dorewa a Unguwar Hotoro, Kawo Da Dukkanin Jihar Kano Baki Daya

Cikin Wani Bincike da Aka Gudanar Ya Nuna Yadda Gidaje da Filaye Sukayi Daraja Tare da Samun Arziki Mai Dorewa a unguwar Hotoro da Kawo a Cewar Wani Dillalin Gidaje da Filaye Mallam Muhammadu.

Yace Ansamu Darajar Kashi 40 cikin 100 Na Gidaje da Filaye Sanadiyar Zuwan Jami’ar Maryam Abacha.

Mallam Muhammad Ya Bayyana Yadda Kasa ta kara Darajar Kashi 30 cikin 100.

A nasu bangaran suma mazauna yankin sun ce tabbas sun samu cigaba, sannan ya’yansu sun samun aiki tare da samun Ingantaccen tsaro titina da hanya tare da Samun wutar lantarki da Ruwan Famfo Sanadiyar Jami’ar Maryam Abacha.

Sojoji sun tarwatsa maɓoyar ƴanbindiga, sun kuɓutar da mutane a Taraba

Ta fuskantar kasuwanci wani Malam Usman Yahaya yace sun sami cigaba sakamakon yadda daliban jami’ar suke sayan kayansu.

Sai kuma Wata yar kasuwa mai suna Angelina nai sayar da masara ta yi bayanin cewa tana samun ciniki sosai ba kamar baya ba

Alh Ibrahim Kalamuwahid Ya Bayyana Cewa Kasuwancinsu ya karu da Kashi 50 cikin Dari.

Suma dalibai sun bayyana farin cikin su da samun gurbin karatu a Jami’ar Maryam Abacha da kuma yadda al’umma Mazauna Yankin ke Musu faran-faran cikin girmamawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...