NNPP ta mayar da martani ga Boniface da ya zargi Kwankwaso da kwace masa jam’iyyar NNPP

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Jam’iyyar NNPP tace ta ga dacewar dole ta yi magana kan munanan kalaman Cif Boniface Aniebonam, tsohon dan jam’iyyar da aka kora.

“Yana da kyau a bayyana cewa korar tasa tare da wasu daga cikin ’yan uwansa, ta kasance ne sakamakon abubuwan da suka yi wadanda suka wuce gona da iri, da kuma dakile ci gaban jam’iyyar gaba daya, kuma sai da aka bi doka Sannan aka koresu daga jam’iyyar*.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran jam’iyyar NNPP na kasa Ladipo Johnson ya sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24.

Yadda akai Rarara ya yi min waƙa – Fatima Mai Zogale

Sanarwar ta ce tun a wancan lokaci Aniebonam da sauran su sun shigar da karrarkin a gaban kotuna domin kalubalantar hukuncin da jam’iyyar ta yanke musamman kan korar su. Sun kuma bukaci kotun da ta tilasta wa INEC ta amince da su a matsayin Sahihancin yan jam’iyyar ta NNPP.

“To sai dai kuma, ya zuwa yanzu, duk irin wannan mataki na shari’a da suka rika dauka ya ci tura, kuma kotuna daban-daban sun yanke shawarar amincewa da jam’iyyar NNPP a matsayin jam’iyyar siyasa, karkashin ingantacciyar jagorancin Dakta Ahmed Aduji”.

Sanarwar ta kara da cewa matakin da ya dace ga Aniebonam da abokan tafiyarsa shi ne su daukaka kara game da hukuncin da kotu ta yanke musu amma sai suka koma yin kalaman batanci, yaudara da kuma karyata ga jagoran jam’iyyar na kasa da kuma Shugabancin jam’iyyar.

Hukumar NEMA ta Bayyana Adadin Wadanda Suka Rasu a Hatsarin Ginin da Afkawa wasu a Kano

Yanzu, Aniebonam na ikirarin mallakar jam’iyyar ne kawai amma wannan ba gaskiya ba ne , kuma hakan ya sabawa dokar. Kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya ya fito karara yayi bayani a kan mallakar jam’iyya da zama yan jam’iyyar, mutum daya ba zai iya mallakar jam’iyyar bajam’iyya ba, sai dai gamayyar mutane.

NNPP na son sanar da jama’a cewa ta bi dukkanin matakai na Shari’a kafin ta kori Boniface daga jam’iyyar ta NNPP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Likitocin Jinya da Ungozoma sun janye yajin aiki – Ministan lafiya

Ƙungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta...

Sarkin Hausawan Arewa, Amb. Balarabe Tatari, Ya Aike da Sakon Ta’aziyyar Buhari da Dantata

Sarkin Hausawan Arewa kuma Ambasadan Zaman Lafiya, Alhaji Balarabe...

INEC ta sanya ranar fara rijistar masu zabe a Nigeria

Hukumar zaɓen Najeriya ta ce nan gaba cikin wannan...