Hukumar NEMA ta Bayyana Adadin Wadanda Suka Rasu a Hatsarin Ginin da Afkawa wasu a Kano

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku tare da jikkata wasu biyu a wani gini mai hawa uku da ya rufta a unguwar Kuntau da ke karamar hukumar Gwale a Kano.

Dokta Nuradeen Abdullahi, kodinetan hukumar NEMA na Kano, ya tabbatar da faruwar lamarin da kuma adadin wadanda suka mutu a ranar Juma’a a Kano.

“Mun sami kiran waya mai cike da damuwa yau da misalin karfe 9:20 na safe daga wani mutum cewa wani gini mai hawa uku da ake ginawa ya ruguje a unguwar Kuntau”.

Iftila’i: Wani Gini ya Fado Kan Magina 12 a Kano

“Ya zuwa yanzu, an ceto mutane biyar, kuma an kai su Asibitin kwararru na Murtala Muhammad, inda aka tabbatar da mutuwar uku daga cikinsu, yayin da wasu biyu suka jikkata suka samu raunuka, kuma suke samun kulawa.” Inji Abdullahi.

Ya kara da cewa har yanzu ana ci gaba da aikin ceto wadanda suka makale a cikin buraguzan ginin.

“Tawagar NEMA da hukumar kashe gobara ta jihar Kano da ‘yan sanda da Red Cross da NSCDC da SEMA da dai sauran su na nan a wurin da lamarin ya faru domin tabbatar da fito da sauran mutanen da suka makale,” in ji Abdullahi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...