Dangane da kokawar da al’umar jihar Kano suke yi kan karancin ruwa, hukumar samar da ruwa ta jihar ta ce hakan ya biyo bayan gyara Famfunan Ruwa na matatarruwa ta Tamburawa da ake yi,shi ne ya gurgunta ayyukan samar da ruwa a wasu bangarori na jihar.
Al’ummomin yankunan da sunayensu ke rubuce a kasa, su ne wadanda matsalar ruwan sha ta shafa a yankunansu.
Don haka da zarar al’amura sun inganta, ruwa zai wadata a dukkanin yankunan.
Don haka Hukumar Ruwa ta Jihar Kano ta yi nadamar duk wata matsala da ta faru sakamakon karancin ruwan da aka samu a wadannan yankuna:
➤ NAIBAWA
➤ U/UKU
➤ KUNDILA
➤ GYADI GYADI
➤ TARAUNI
➤ KARKASARA
➤ NASSARAWA
➤ DANGAURO
➤ TUDUN BAYERO
➤ GARIN TAMBURAWA.
Duk da haka, wasu yankuna suna ci gaba da samun ruwa ba tare da katsewa ba musamman, ƙarƙashin Yankunan da aka lissafa kamar haka:
➤ PANSHEKARA
➤ DORAYI
➤ GASAU
➤ GAIDA
➤ SAMEGU
➤ SABUWAR GANDU
➤ SHARADA
➤ SABON TITI
➤ KOFAR FAMFO
➤ KOFAR NAISA
➤ KOFAR DANAGUNDI
➤ KABARA
➤ GIDAN SARKI
➤ GWALE
➤ SABUWAR KOFA
➤ AISAMI
➤ GAURON DUTSE
➤S/MAINAGGE
➤ BUK OLD SITE
➤ DUKAWUYA
➤ DAWANAU
➤ MULTARA
➤ BACHIRAWA
➤ KURNA
➤ REJIYAR LEMO da sauransu.
Sanarwar daga shugaban hukumar samar da ruwan sha ta jihar Kano Engr. Garba Ahmad Bichi .