CBN ya bayyana matakan da yake bi har Dala take karyewa a Nigeria

Date:

 

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) Yemi Cardoso ya ce matakan da suka ɗauka na biyan bashin dalolin da ake bin su sun sa naira ta kasance kuɗin da ya fi samun tagomashi a duniya a yanzu haka.

Cardoso ya bayyana haka ne ranar Asabar bayan kammala taron da Bankin Duniya da Asusun Bayar da Lamuni na IMF suka gudanar a birnin Washington DC na Amurka.

Yadda jarumar kannywood Aisha Humaira ta yi alkawarin magance matsalar ruwa a Kano

A watannin baya bayan nan darajar kuɗin Nijeriya ta yi matuƙar karyewa idan aka kwatanta da dalar Amurka lamarin da ya haddasa tashin farashin kayayyaki da kuma ƙara tsadar rayuwa a tsakanin ƴan ƙasar.

Sai dai matakan da CBN ya ɗauka ciki har da biyan bashin dala biliyan bakwai da ake bin sa da kuma yin garambawul a kasuwar canji sun taimaka wurin farfaɗowar darajar naira.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta Rufe Wani Asibiti Mai Zaman Kansa Saboda Karya Doka

“Naira ta kasance kuɗin da ya fi samun tagomashi a duniya a watan Afrilu… kasuwarmu ta kuɗaɗen waje tana samun babban tagomashi inda ta samu darajar da ba a taɓa ganin irin ta ba a cikin shekaru bakwai,” in ji shi.

“Bashin da muka biya na kuɗin ƙasashen waje ya bai wa masu zuba jari da ƴan kasuwa da sauran abokanmu ƙarfin gwiwa, abin da ya sa suka ƙara hada-hada a kasuwar musayar kuɗi ta Nijeriya,” a cewar Cardoso.

Sai dai Gwamnan CBN ya ce ba za su saki jiki ba domin suna sane da irin ƙalubalen da tattalin arzikin Nijeriya yake fuskanci ciki har da ƙarin hauhawar farashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...