Rashin katabus: Gwamnatin Kano ta baiwa Pillars wa’adin wasanni uku na su farfaɗo da ƙoƙarin su

Date:

 

Gwamnatin jihar Kano ta bayar da wa’adin wasanni uku ga mahukuntan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars domin dawo da ƙoƙarin ta da samun nasara a jere.

Mukaddashin Kwamishinan Matasa da Wasanni, Hamza Safiyanu Kachako ne ya ba da wa’adin, biyo bayan rashin kokari da kungiyar ke yi a kwanakin nan a gasar Firimiyar Najeriya ta kakar 2023/24.

Kano Pillars, wadda aka fi sani da “Sai Masu Gida,” ta fuskanci koma baya a wasanni na baya-bayan nan, inda ta sha kashi a hannun Bendel Insurance na Benin da ci 2-1. Kafin rashin nasarar kungiyar ta sha fama da rashin nasara a jere da suka hada da rashin nasara a hannun Shooting Stars da ci 1-2 da kuma rashin nasara da Enyimba International da ci 5-0.

Ya Kamata Gwamnati ta Fara Tilastawa Yan Kasuwa Don su Sauke Farashin Kayan su – Falakin Shinkafi

Sai dai Kwamishinan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar, karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf na taimakawa Kano Pillars baya domin samun nasara.

Gwamnan Kano ya chanzawa wasu daga cikin Kwamishinonin sa ma’aikatu

Sai dai ya bayyana cewa dole ne a dauki kwararan matakai don dawo da kungiyar zuwa ga nasara, inda ya bayyana cewa gwamnati ba za ta sa ido kan yadda ƙungiyar ta Kano ke tabarbare wa ba.

Daga nan ne aka bukaci mahukunta da ma’aikatan kungiyar ta Kano Pillars da su sauya al’amura a wasanni uku masu muhimmanci da za su fara da wasan da za su kara da kungiyar Gombe United a ranar Lahadi, 21 ga Afrilu, 2024, a filin wasa na Sani Abacha, Kano.

Za a kuma ta buga wasa a waje da Akwa United da kuma karawar gida da Doma United ta Gombe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abun Alkhairin da mataimakin gwamnan Kano ya yi min ba a taba yin min shi a duniya ba – Kabiru D Bello

Tsohon Dan takarar shugaban karamar hukumar Gwarzo Alhaji Kabiru...

Gidajen Wasanni a Kano sun bi ka’idojin da muka sanya musu yayin bikin sallah – Abba El-Mustapah

Daga Rahama Umar Kwaru   A wani bangare na kokarin tabbatar...

Mijina bai yi sata ba kuma kudin da ya tara wa Nijeriya duk an wawashe su – Maryam Abacha

    Maryam Abacha, matar marigayi Janar Sani Abacha, tsohon shugaban...

Matsalar Ruwan: Shugaban K/H Wudil ya ba da Umarnin gyara rijiyoyin burtsatse 100 a yankin

Daga Rahama Umar Kwaru   Shugaban karamar hukumar wudil Hon. Abba...