Yadda Wani Mutum Ya Yi Kokarin Hallaka Kansa A Masallacin Harami

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Jami’an tsaro na musamman da ke kula da Masallacin Harami da ke Makkah sun fara gudanar da bincike a kan wani mutum da ya fado daga benen saman masallacin.

Kadaura24 ta rawaito An kai mutumin asibiti domin ya sami kulawar da ta dace ba tare da bayyana ko Dan wacce kasa ce ba.

Ka Yi Aikin Dake Gabanka Ka Rabu Da Ganduje – Kwankwaso Ya Fadawa Abba Gida-gida

Rundunar ta musamman mai kula da tsaron masallacin Al Haram ta bayyana a shafinta na “X” wato Twitter cewa “an kammala duk abubunwan da suka dace,” ba tare da bayyana karin bayani kan lamarin ba.

Yanzu-yanzu: Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi sabbin nade-nade a Kano

Idan za’a iya tunawa a shekarar 2018, wani mahajjaci mai shekaru 26 ya kashe kansa a Masallacin Harami, lamarin da ya haifar da firgici da fargaba a tsakanin alhazai da masu ibada a Masallacin.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Makkah ta kafafen yada labarai ya bayyana a watan Yunin 2018 cewa jami’an tsaro sun fara gudanar da bincike kan lamarin inda wani mahajjaci ya fado da baya daga rufin Mas’a zuwa farfajiyar kasa, lamarin da ya yi sanadin rasa rayuka a bayan Maqam.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Hukumar kula da aikin 'yan sanda na Kasa (POLICE SERVICE...

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya...