Tinubu ya Sauyawa Lawan Jafaru Isa Mukami

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin sabbin shugabannin hukumar kula da Almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta.

Ya zabi Birgediya-Janar Lawal Ja’afar Isa (mai ritaya) ya zama shugaban hukumar gudanarwar hukumar, yayin da Dr Idris Muhammad Sani zai zama babban sakataren zartarwa na hukumar

Ja’afar Isa shugaba ya taba rike mukamin gwamnan mulkin soja na jihar Kaduna daga 1993 zuwa 1996.

Dangote na ciyar da mutane Dubu Goma a Kano Kullum a watan Ramadan, Ya raba buhunan shinkafa Miliyan 1 a Nigeria

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da masharci na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Tashe: Rundunar yan sandan Kano ta bayyana shirin ta na yakar masu tada hankali

Dr Muhammad Sani yana da digiri na biyu da na uku a fannin ilimin addinin Musulunci. Ya kasance a lokuta daban-daban a matsayin Darakta-Janar na Makarantar Al-Iman Lafia, ya kuma taba zama Kwamishinan Ilimi jihar Yobe da dai sauransu.

ShugabaTinubu ya ce, yana sa ran sabbin shugabannin da aka nada za su yi amfani da gogewarsu wajen gudanar da hukumar, domin tabbatar da cewa gwamnatinsa na kokarin ilimantar da yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya da Almajirai don inganta rayuwar su .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...