Abba Gida-Gida ya Saukewa Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Kano Kabakin Arziki

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya raba kayan abinchi ga daukacin ma’aikatan dake aiki a gidan gwamnatin jihar, a wani bangare na tallafin watan azumin Ramadan.

Kadaura24 ta rawaito cewa kowanne ma’aikaci ya rabauta da babban buhun shinkafa 50kg da katan din makaroni da gero kwano 10 da kuma kudi Naira dubu 10 na cefane.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Shahararren Mawakin Hip Hop Ya Karɓi Musulunci A Amurka

Da yake kaddamar da shirin bada tallafin, gwamna Abba Kabir Yusuf yace ya basu tallafin ne domin su gudanar da ibadu watan azumin ramadan cikin nutsuwa tare da iyalansu.

” Kuna da matukar muhimmaci a wajen tafiyar da harkokin gudanarwa na gwamnati , don haka ya kamata kuma mu kyautata muku don ku ji dadin cigaba da ibadar azumin watan Ramadana”. A cewar Abba Kabir Yusuf

Umarnin Shigo da Kayan Abinchi shi Yan Nigeria Suke Bukata – Waiya ya fadawa Tinubu

Gwamnan yace bayan ga ma’aikatan gidan gwamnatin jihar kano suma sauran al’ummar jihar kano zasu amfana da tallafin kayan abinchi a cikin wannan wata, Mun samar da tallafin kayan abinchi ne domin saukakawa al’umma saboda mawuyacin halin da mutane suke ciki.

Wasu daga cikin ma’aikatan gidan gwamnatin da jaridar kadaura24 ta zanta da su sun baiwa jindadinsu da kabakin alkhairin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya sauke musu a wannan wata mai albarka.

Sun kuma ce tallafin zai kara musu kwarin gwiwar cigaba da gudanar da aiyukansu kamar yadda ya kamata ba tare da gajiyawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...