Ramadan: Sarkin Kano ya bukaci ‘yan kasuwa da su rage farashin kayan abinci

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi kira ga ‘yan kasuwa musamman masu sayar da kayan masarufi da su rage farashin kayan abinci da sauran kayayyaki domin baiwa talakawa damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

Sarkin ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Zariya a lokacin cin abincin rana da aka shirya bayan kaddamar da wani littafi mai suna: “Dauloli a Kasar Hausa” na Farfesa Sa’idu-Mohammed Gusau.

 

Ado Bayero ya kuma shawarci ’yan Najeriya masu hannu da shuni da su rika taimakawa marasa galihu a lokacin azumin Ramadan.

Ramadan: Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 na Kayan Abinchi a Zamfara

Ya kuma yi addu’ar Allah subhanahu wata’ala ya nuna mana wannan wata mai alfarma cikin koshin lafiya ya kuma karbi addu’o’in da al’umma zasu gudanar.

Sarkin ya yabawa mawallafin littafin, da ya bayar da cikakkun bayanai kan masarautun Hausawa a Kano, Katsina, Zamfara, Kebbi da Zazzau da dai sauransu.

Muhimmiyar Sanarwa Daga Rundunar Yan Sandan Jihar Kano

“An yi cikakken bayani kan tsarin gudanar da mulki na kowace masarauta, sana’o’insu, ka’idoji da dabi’unsu,” inji shi.

Wanda ya duba littafin Farfesa Ahmed Zaria na Jami’ar Jihar Kaduna ya ce littafin mai shafi 356 yana da babi bakwai.

Farfesa Ahmad Zariya ta ce littafin ya ba da cikakken labari da tarihin masarautun Hausa, siyasarsu, gudanar da mulki, ka’idoji da kuma dabi’u daga kafuwarta zuwa yau.

Ya kara da cewa akwai bukatar kowanne dalibi dake bincike a fannin Ilimin harshen Hausa da tarihinsu ya mallaki littafin littafin don kyautata binciken sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...