Kar Ku Rika Biyan Kudin Gyaran Transfoma —Kamfanin JED

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Jos (JED) ya shawarci abokan huldarsa a Jihar Gombe da kada su biya kowa kudin gyara na’urar taransfoma a yankunansu.

Babban jami’in tsaro na JED, Musa Abdullahi, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Litinin cewa, ba hakkin kwastomomi ba ne su gyara taransfoma idan ta lalace.

Abdullahi ya ce ana sa ran jama’a su kai rahoto ofishin JED mafi kusa a duk lokacin da na’urar taransifoma ta samu matsala, kuma kada su biya wani jami’inta kudin gyara.

Ramadan: Sarkin Kano ya bukaci ‘yan kasuwa da su rage farashin kayan abinci

Ya ce ba daidai ba ne a nemi al’umma su ba da gudummawar kudi don gyara ko canza taransfomarsu da ta lalace, hasali ma yaudara ce da kamfanin ba zai lamunta ba.

Jami’in ya shawarci al’ummar jiha da su kai rahoton duk wani ma’aikacinsu da ya nuna irin wannan bukata domin daukar matakin da ya dace.

Ya ce “Ba ma karbar kudi daga hannun al’umma don gyara tiransifoma don haka babu wanda ake tsammanin zai biya.

Muhimmiyar Sanarwa Daga Rundunar Yan Sandan Jihar Kano

“Duk ma’aikacin da ya je wurin al’umma karbar kudi a gida-gida ko a kan titi, yaudara ce kuma mun haramta hakan.

“Idan kuna ganin ba za ku iya jira a gyara taransfoma ba, sai ku rubuta wa Manajan Darakta ta hannun Manajan Yankinku cewa kuna son tallafa wa kamfanin don radin kanku ba tilasta muku aka yi ba.

Abdullahi ya kuma yi kira ga al’ummar Gombe da su mara wa kokarin kamfanin na kare wutar lantarki a jihar.

Sannan ya yi kira da kada a rika cin zarafin jami’an JED da ke bakin aiki, yin hakan laifi ne.

Aminiya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...