Gwamnatin Kano ta Sanya Ranar Ziyartar Daliban Makarantun Kwana

Date:

Daga Ibrahim Abubakar Diso

 

Gwamnatin jihar Kano tace ta amince iyayen ‘ya’yan su ke makarantu a makarantun kwana a jihar da su ziyarci daliban a ranar Asabar 2 ga Maris, 2024.

Kadaura24 ta rawaito hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan wayar dakan al’umma na ma’aikatar Ilimi ta jihar kano Balarabe Abdullahi kiru ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Yanzu-yanzu: CBN ya sanar da matakan dakile hauhawar farashin Dala a Nigeria

Sanarwar tace iyayen daliban zasu iya fara Ziyartar ya’yan nasu tun daga karfe 9:00 na safe zuwa 5:00 na yamma a ranar da aka sanya.

A cewar sanarwar an umurci iyayen daliban da su da su tabbatar da bin ka’idojin da suka shafi ziyarar.

Yan Sanda Sun Kama mutane 9 Masu Chanjin kudaden Waje ba Bisa ka’ida ba

Sai dai sanarwar ta ruwaito kwamishinan ma’aikatar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana jin dadinsa da irin goyon baya da hadin kai da aka saba baiwa ma’aikatar tare da yi wa daliban da iyayensu fatan kammala ziyarar cikin nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...