Da dumi-dumi: Kotu ta sake bada sabon Umarni akan Mawaki Ado Gwanja

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babbar kotun jihar Kano mai Lamba 5 dake zamanta a sakatariyar Audu Bako ta haramta sanya wakokin Chass da Asosa na mawaki Ado Gwanja.

Da take zartar da hukunci mai shari’a Aisha Ibrahim Mahmud ta bayar da umarni haramta sanya wakokin a dukkan taruka na jama’a har zuwa lokacin da hukumar tace Fina-finai zata kammala tantancesu.

Cikakken Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Haramtawa Ado Gwanja Yin Waƙa, Bayan Kama Shi

Umarnin na kunshe ne cikin wata takarar Kara mai lamba k/m/383/2023, Inda a ciki takardar mai Shari’a Aisha Mahmoud ta ce ta kori karar da ado Gwanja ya shiga yana kalubalen ta wata kotun Shari’ar Musulunci dake Bichi da cigaba da sauraron karar da zauren malaman kano suka shigar akan sa.

Yan Sanda Sun Kama mutane 9 Masu Chanjin kudaden Waje ba Bisa ka’ida ba

Tun da farko dai Ado Gwanja ne ya shiga da karar a gaban babbar kotun jihar kano yana Kalubalantar Umarnin da kotun Shari’ar Musulunci dake Bichi ta bayan na a kamo shi.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a jiya litinin kotun ta bada umarnin a kamo mawaki ado Gwanja tare kuma da Haramtawa mawakin sake yin waka har sai kammala bincike kan Shari’ar da zauren malaman jihar kano suka kai shi, sakamakon yin wata waƙa mai suna WAR.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...