Zargin Juyin Mulki: Helkwatar tsaron Nigeria ta Magantu ta Batu

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Hedikwatar tsaro ta Najeriya ta yi fatali da zargin da wata kafar yaɗa labarai ta intanet ke yaɗawa kan iƙirarin cewa an sanya masu tsaron fadar shugaban ƙasa a shirin ko ta kwana bayan zarge-zargen da ake yi kan fargabar kifar da gwamnati.

Wata sanarwa da muƙaddashin daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron, Brigadiya Janar Tukur Gusau ya ce an ankarar da su game da wani rahoto da aka wallafa a intanet a ranar 25 ga watan Fabarairun 2024 da ke iƙirarin cewa masu tsaron fadar shugaban ƙasa na cikin shirin ko ta kwana sakamakon wasu alamu da ke janyo fargabar yin juyin mulki a Najeriya.

“Rahoton ya kuma ce zargin ya janyo yin taron gaggawa tsakanin shugaba Bola Tinubu da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa.

Kungiyar Kwadago ta bayyana matakin da zata dauka idan aka kaiwa ya’yanta hari yayin zanga-zanga

Hedikwatar tsaron ta ƙaryata labarin inda ta ce an tsara masu tsaron fadar shugaban ƙasa su kare fadar da kuma babban birnin tarayya da kewayenta.

A cewar hedikwatar tsaron, a kullum jami’an tsaron da ke fadar shugaban ƙasa na cikin shirin ko ta kwana domin sauke nauyin da aka rataya a wuyansu.

Marubucin Fim din Labarina Ya yiwa yan kallo Martani game da Shirin na Wannan makon jiya

Hedikwatar ta kuma yi waiwaye kan yadda babban haftsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya sha nanata ƙudurin jami’an sojin Najeriya na kare martabar dimokradiyyar ƙasar.

A don haka hedikwatar tsaron ta yi kakkausar suka kan zargin inda ta buƙaci jama’a su yi watsi da shi.

Hedikwatar ta kuma yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukan mataki kan jaridar da ta wallafa labarin saboda mataki ne na rashin nuna kishin ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Magance sheye-shaye ne kadai zai kawo karshen matsalar tsaro da talauci a Nugeria – Shugabar LESPADA

Daga Usman Usman   Ambassador Maryam Hassan shugabar kungiyar wayar da...

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Daga Isa Ahmad Getso ‎ ‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers ta bayyana...

Rahoto: An kwantar da Buhari a ICU a Landan

  Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin...

Kacibus: A karon farko an hadu tsakanin Gwamnan Abba da Sarki Aminu Ado a Madina

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   A karon farko an hadu tsakanin...