EFCC ta Kama Mutane 11 bisa Zarginsu da Sayar da Sabbin Kuɗi a Kano

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Jami’an hukumar yaki da masu yi wa tattalin Arzikin kasa zagon kasa EFCC, sun kama wasu mutane 11 (11) da ake zarginsu da, sayar da sabbin takardun Naira don kasuwanci.

An kama su ne a ranar Litinin, 19 ga Fabrairu, 2024, biyo bayan wasu bayanan sirri da suka samu, inda suke rufe fuskokin suna sayar da sabbin takardun kuɗin a kan titin Legas, daura da babban bankin Najeriya, Kano.

ECOWAS ta Bayyana Dalilan da Suka sa Ta Janyewa Nijar, Mali da Burkina Faso Takunkumi

Su dai masu waccan sana’ar suna sayar da sabbin takardun kuɗin ne musamman ga wadanda suke biki ko wasu al’amura .

Wadanda ake zargin sun kware wajen sayar da takardun kudi na Naira. Don haka aka kama wasu mutane 5 a cikin masu sayar da sabbin takardun Naira ga jama’a.

An kuma kama wasu ma’aikatan banki guda shida da ake zargin suna sayar da takardar kudin Naira ga masu siyar da sabbin kuɗin.

Nan ba da jimawa ba za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...