Yadda wasu Matasa suka daka wa motocin Abinchi wawa a jihar Neja

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Rahotanni da ga jihar Neja na baiyana cewa wasu ɓatagari sun tare tireloli makil da kayan abinci da kayan abinci a yankin Suleja, lamarin da ya sa sojoji suka yi harbi sama don korar su a yau Alhamis.

Wani ganau, Alhassan Abdullahi, ya shaida wa wakilin Daily Trust cewa ɓatagarin, wanda suka kona tayoyi sun tare tirelolin da ke tahowa daga Abuja zuwa Kaduna.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Tarayya ta Dauki Matakan Rage Tsadar Iskar Gas a Nigeria

Ya ce sun sace buhunan kayan abinci iri-iri, musamman shinkafa kafin sojoji su isa wurin.

Yadda kamfanonin Kirifto ta Haddasa Tashin Farashin Dala a Nigeria

“Allah Ya sanya sojoji sun isa wurin sannan suka fara harbin bindiga a iska don tsoratar da ɓatagarin. Amma ko da hakan, da yawa daga cikinsu sun tafi da buhunan shinkafa da katan-katan na taliya da sauran kayan abinci.”

Wannan ci gaban dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da wahalhalun da kasar ke fama da shi wanda ya haifar da zanga-zanga a sassa daban-daban na kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...