Kawaje Yayi Murnar Cika Shekara 50 Akan Karaga Da samu Cigaba a Yankin

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Mai Unguwar Kawaje, dake Karamar hukumar Nasarawa a jihar kano, Alhaji Umar Ado, ya kasance cikin farin ciki da murna, yayin da ya cika Shekaru 50 a kan karagar mulki, inda ya tuna da rashin jin dadi da ya kasance a lokacin da yake mulkar akalla gidaje 500.

Da yake jawabi a yayin bikin, shugaban kwamitin gudanarwa wanda kuma shi ne shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta kasa, Dokta Bature AbdulAziz, tare da Sakatarensa, Alhaji Dahiru Musa, ya ce cikin shekaru 50 da suka gabata a karkashin jagoranci da sa ido mai Unguwar ta kawaji an sami cigaba ta fannoni daban-daban a yankin .

Hukumar Gidan Gyaran Hali ta Kano ta Magantu Kan Bacewar Murjar Kunya a Gidan Yari

Bature AbdulAziz, ya ce a shekaru 50 da suka gabata babu wani Kamfani ko wata babban Kasuwa da ke gudanar da harkokinsu a yankin, amma a yau akwai kamfanoni sama da 50 da ke aiki a kawaji, yayin da akwai sama da Makarantu sama da 50 kuma suna gudanar da ayyukan bada ilimi a duk a yankin.

Sakataren kwamitin, Dahiru Musa, ya yi nuni da cewa saboda hadin kai da kaunar juna da aka samu a yankin ya sa mutane da yawa suka bada gudunmuwa har aka sami nasarar yin wannan taro na cikar mai unguwar kawaji shekaru 50 akan karagar Mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Ayyana Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gobe Juma’a, 12 ga...

INEC ta yi Allah-wadai da masu yakin neman zabe tun kafin lokaci ya yi

Hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta yi Allah wadai...

Yin rijistar katin Zabe zata taimaki addinin musulunci da musulmai – Mal Usman Mai Dubun Isa

Shahararren mai yabon Manzon Allah (S A W) Malam...

Tinubu y ba da umarnin sake Karya farashin kayan Abinci a Nigeria

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bai wa wani...