Da dumi-dumi: Kotun Shari’ar Musulunci ta Kwace Kaddarorin Sha’aban Saboda Bashi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci ta 1 da ke zamanta a GRA, Zariya, Jihar Kaduna, ta umarci Hon Sani Sha’aban, tsohon dan takarar Gwamnan Jihar Kaduna a karkashin Jam’iyyar APC, da ya biya bashin $709,238 da Naira miliyan 11.2 da Alhaji daya. Umar Faruk Abdullahi yake binsa .

Khadi, Alhaji Ishaq Madahu, a yayin da yake yanke hukuncin, ya kuma bayar da umarnin a kwace kadarorin Hon Sha’aban da aka yi amfani da su wajen yarjejeniyar bashin .

Bugu da kari, kotun ta bayar da umarnin a gaggauta nemo masu siyan kadarorin da ya bayar don warware basussukan, inda ta jaddada cewa idan darajar dukiyar da aka makala ta zarce adadin lamunin, to sai a mayar wa wanda ake kara (Sha’aban) da sauran kudinsa.

Aminu Dantata ya Bayyana Ra’ayinsa Kan Batun Sauya Tsarin Shugabanci a Nigeria

Kotun ta kuma umurci Sha’aban ya yi musu ciko idan darajar kadarorin ba ta kai adadin kuɗin da ake binsa ba.

Tattalin arziki: Tinubu Ya Gana da Gwamnoni

Daily Trust ta rawaito Lauyan wanda ya shigar da kara, Kabir Momoh, ya bayyana jin dadinsa da hukuncin, yayin da lauyan wanda ake kara, Nasir Sa’id, ya ce wanda ya ke karewa bai bashi damar yin magana da manema labarai ba akan lamarin.

Idan dai ba a manta ba a shekarar 2018 ne Honarabul Sani Mahmud Sha’aban (Dan Duran Zazzau) da Alhaji Umar Faruk Abdullahi suka rattaba hannu kan yarjejeniyar lamuni don ganin an sako shi daga wata matsala da ya samu a Dubai (UAE) a waccan shekarar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar kula da almajirai ta Kasa ta kaddamar da yiwa almajirai Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...