ECOWAS ta Mayar da Martani Kan Ficewar Mali, Burkina Faso, Nijar daga Kungiyar

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas ta ba ta samu sanarwa a hukumance ba game da ficewa mambobinta uku Nijar Mali da Burkina Faso ba.

Ƙasashen uku sun sanar da ficewarsu daga ƙungiyar ne cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da aka karanta a gidan talabijin, inda suka zargi ƙungiyar da gazawa a taimaka musu wajen yaƙi da ta’addanci da kuma matsalar tsaro.

Tausayi da karamcin Dangote ne suka sanya ya tsere wa tsara a harkokin kasuwanci a Najeriya da Afirka – Yan Kasuwa

To sai dai cikin wata sanarwar da Ƙungiyar ta fitar da maraicen ranar Lahadi, ta ce babu wata katarda da ƙasashen suka aike mata bisa wannna aniya tasu.

Ecowas ɗin ta ce tana aiki da waɗannan ƙasashen uku domin maido da su kan turbar dimokraɗiyya.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƙasashen uku na da matuƙar muhimmanci ga ƙungiyar, don haka take ƙoƙarin ganin ta lalubo hanyoyin warware matsalolin da ƙasashen ke fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...