ECOWAS ta Mayar da Martani Kan Ficewar Mali, Burkina Faso, Nijar daga Kungiyar

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas ta ba ta samu sanarwa a hukumance ba game da ficewa mambobinta uku Nijar Mali da Burkina Faso ba.

Ƙasashen uku sun sanar da ficewarsu daga ƙungiyar ne cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da aka karanta a gidan talabijin, inda suka zargi ƙungiyar da gazawa a taimaka musu wajen yaƙi da ta’addanci da kuma matsalar tsaro.

Tausayi da karamcin Dangote ne suka sanya ya tsere wa tsara a harkokin kasuwanci a Najeriya da Afirka – Yan Kasuwa

To sai dai cikin wata sanarwar da Ƙungiyar ta fitar da maraicen ranar Lahadi, ta ce babu wata katarda da ƙasashen suka aike mata bisa wannna aniya tasu.

Ecowas ɗin ta ce tana aiki da waɗannan ƙasashen uku domin maido da su kan turbar dimokraɗiyya.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƙasashen uku na da matuƙar muhimmanci ga ƙungiyar, don haka take ƙoƙarin ganin ta lalubo hanyoyin warware matsalolin da ƙasashen ke fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...