Burkina Faso da Mali da Nijar za su fice daga ECOWAS

Date:

 

Uku daga cikin ƙasashen da sojoji suke jagoranta a yammacin Afrika sun ce za su fice daga ƙungiyar raya tattalin azriƙin yankin ta ECOWAS saboda takunkumin da kungiyar ta sanya musu.

Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun sanar da haka ne ta cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da aka karanta a gidan talabijin, suna cewa ECOWAS ta gaza taimaka musu wajen yaƙi da ta’addanci da kuma matsalar tsaro.

Jarumar Hadiza Gabon Ta Yi Martani ga Masu Magana Kan Ramarta

“Bayan shekaru 49, gwarazan al’umar ƙasashen BUrkina Faso da Mali da Nijar sun yi takaicin yadda ECOWAS ta sauka daga kan turbar da aka kafa ta, kamar yadda Kanar Amadou Abdramane, shugaban da ke jagorantar sojin da suka yi juyin mulki a Nijar ya karanta.

ECOWAS ta ƙaƙaba wa ƙasashen uku takunkumai tare da dakatar da su daga daga ƙungiyar, biyo bayan kwace iko da sojoji suka yi a jerin juyin mulkin da suka yi, abin da ya haifar da fargaba ta ɓangaren siyasa a Sahel.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...

NNPPn Kano ta bayyana matsayar Kwankwaso kan batun yi wa Tinubu mataimaki a 2027

Shugabanin bangarori biyu na jam’iyyar NNPP a jihar Kano,...

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...