An rantsar da Ododo a matsayin sabon gwamnan Kogi

Date:

 

 

Usman Ododo ya sha rantsuwar kama aiki a matsayin sabon gwamnan jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya, bayan nasarar lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar cikin watan Nuwamba.

An gudanar da bikin rantsuwar ne a Lokoja babban birnin jihar ranar Asabar da rana, inda aka rantsar da shi tare da mataimakinsa, Salifu Joel Oyibo.

Komai Girmanka Indai ka Shigo APC a Karkashina Zaka Zauna – Ganduje

Mista Ododo wanda ɗan jam’iyyar APC ne zai maye gurbin Yahaya Bello wanda ke kammala wa’adin mulkinsa na biyu.

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima, da gwamnan jihar Yahaya Bello da wasu jiga-jigan jam’iyyar APC, na daga cikin mutanen da suka halarci bikin rantsuwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...