Komai Girmanka Indai ka Shigo APC a Karkashina Zaka Zauna – Ganduje

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa duk wani dan jam’iyyar APC a yanzu a karkashin sa yake saboda shi ne shugabanta na kasa a yanzu.

” Kada ka ji tsoro idan wani ya zo cin arziki a gidanka, shin da ka je kaci arziki a gidanka shi da ya zo yaci arziki a gidanka wanne ka fi so? , Ai mai shi shi yake da abun bayarwa, marashi shi ne mai neman wurin shiga”.

Kadaura24 ta rawaito Dr. Abdullahi Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da shugabannin kungiyoyin jam’iyyar APC a Ofishin Support Group dake Kano.

Gwamnan Kano Abba Kabir ya Magantu Kan Kiran da Ganduje Yayi Musu na Komawa APC

” Menene aikin shugaban jam’iyyar APC na kasa ? Aikine na jam’iyya a jihar kano kawai ? Jihohi 36 da Abuja duk inda naje nine yallabai nine alasabbanani, nine Sheikh, duk inda naje nina alangoburo, saboda haka na zaga kasar nan ina kiran gwamnoni su shigo jam’iyyar APC don mu samu karuwa, to meye laifi idan na yi haka a jihata ta kano?. Ganduje ya fada

Shugaban jam’iyyar Wanda tsohon gwamnan jihar kano ne ya ce ya sami nasarar shigo da ‘yan kananan jam’iyyu cikin har da NNPP a jihar Bauchi, “don haka a kano ma, Ina rokon yan Jam’iyyar NNPP dukkanin su da su ajiye kayan kwari su zo Inda za’a Adana musu shi a furji don kar su lalace”.

Hakikanin Yadda Siyasar Kano Zata Kasance a 2027 – Daga Bashir Hayatu Gentile

” Yanzu laifi ne Dan na kirawo yan Jam’iyyar NNPP na jihar kano su dawo APC, ai wanda yake da shi shi ake roko, wanda yake da shi shi yake bayarwa, saboda muna rokon su su auna cewa Shugabancin kasar nan a jam’iyyar zai samu?, To saboda kiransu su dawo jam’iyyar APC ai abun alfahari ne mu a wajen mu don haka mu kari muke nema, kuma kamar yadda na fada muku indai ka shigo jam’iyyar ko kai jagorane to nine shugabanka”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...