Tinubu Ya Magantu Kan Batun Dauke Fadar Shugaban Kasa Daga Abuja

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai bai wa shugaban Najeriya Bola Tinubu shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya ce shugaban kasar ba shi da aniyar ɗauke babban birnin tarayyar ƙasar daga Abuja zuwa Legas.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, ranar Laraba, Onanuga ya ce masu yada jita-jita ne ke yaɗa maganar domin jan hankalin al’umma gare su.

Hukumar Hisbah Tana Neman Wasu Taurarin TikTok Guda 6 Ruwa a Jallo

Wannan na zuwa ne bayan matakin da gwamnatin tarayyar ƙasar ta ɗauka na mayar da wasu ɓangarori na Babban bankin Najeriya da kuma Hukumar kula da filayen jiragen sama na ƙasar zuwa Legas, daga Abuja.

Lamarin da ya janyo ƙorafi da kiraye-kiraye daga wasu ƙungiyoyi na wasu ɓangarorin ƙasar, inda suka yi zargin cewa tamkar wani mataki ne aiwatar da wata ‘manufa ta daban.’

Hadewar NNPP Kwankwasiyya da APC a Kano Sabuwar Dambarwar Siyasa ta Kunna Kai

Onanuga ya ce matakin mayar da wani sashi na ma’aikatar FAAN bai kamata ya ja hankalin mutane da yawa ba saboda jihar Legas ita ce cibiyar kasuwanci kuma cibiyar sufurin jiragen sama a Najeriya saboda haka ya ce har yanzu FAAN za ta ci gaba da kasancewa a Abuja.

“Akwai ma’aikatu da yawa da ba a Abuja suke ba dangane da aikinsu kamar NIMASA da take Legas. Haka kuma NPA da kuma hukumar kula da sufurin ruwa (NIWA) da ke Lokoja.’

Sanarwar dai ta ƙara da cewa bai kamata a siyasantar da lamurran gwamnati ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yan sanda a Kano sun lashi takobin samar da ingantaccen tsaro a ranar Takutaha

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori,...

Gwamnatin Kano Ta Ayyana Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gobe Juma’a, 12 ga...

INEC ta yi Allah-wadai da masu yakin neman zabe tun kafin lokaci ya yi

Hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta yi Allah wadai...

Yin rijistar katin Zabe zata taimaki addinin musulunci da musulmai – Mal Usman Mai Dubun Isa

Shahararren mai yabon Manzon Allah (S A W) Malam...