Baiwa Kananan hukumomin Hakkinsu Zai Magance Matsalolin da Dama a Nigeria – Muhd Mustapha

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

Wani Masani Dr. Muhammad Mustapha Yahaya wanda kuma shi ne shugaban kungiyar wanzar da dimokaradiyya da kawo cigaba da Magance Matsalolin tsaro Wanda akafi Sani da Action Group da dispute resolution yace baiwa Kananan hukumomi kudadensu zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro, talauci da yawan rashin aikin yi da ake fama da shi a Nigeria.

Dr. Muhammad Mustapha ya bayyana hakan ne yayin wani taro na masu ruwa da tsaki akan yadda Kananan hukumomin zasu sami yanci kasu wanda kungiyar ta shiya a shirya Masarautar Bichi.

” Rashin Adalci ne hana kananan hukumomi kudadensu, kuma hakan baya haifar da da mai ido, idan akai la’akari da tarin matsalolin da hakan ke haifarwa, don haka muke kira ga duk masu ruwa da tsaki da yi abun da ya dace don fitar da al’umma daga talaucin da aka kakaba musu”. Inji Dr. Muhammad

Cikakken Bayani da Dalilin Yadda aka Gurfanar da Danbilki Kwamanda a Kotu

Yace sun shiya taro ne domin lalubo hanyoyin da za’abi don gani Kananan hukumomin sun samin yancin cin gashin kansu daga wajen gwamnonin jihohi.

Kungiyar ta gayyaci masu ruwa da tsaki Kamar Kungiyoyi Ma’aikatar irin Kungiyar Ma’ikatan Kananan hukumomin, Mallam makarantan firemare, dagatai masu unguwani da Limamai da Sauran Kungiyoyi Mata da Matasa.

Siyasar Kano: Tinubu Ya Baiwa Kwankwaso da Ganduje Umarni

Wasu daga cikin wanda suka hallaci mahalci taro da suka hadar da Mallam Murtala Waire Wanda shine Shugaban Kungiyar Ma’ikatan Kananan hukumomin na Karamar hukumar Bichi da shugabar Kungiyar Mata Mallama Aisha sun bayana cewa baiwa kananan hukumomin yancinsu, zai taimakawa masu jama’a na kasa su fita daga kuncin rayuwar da suke ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...