Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli Ta Yanke Hukuncin Kan Shari’ar Zaɓen Gwamnan Gombe

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Kotun koli ta yi watsi da karar da dan takarar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Nafiu Bala ya shigar kan zaben Muhammad Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan jihar Gombe.

Kwamitin alƙalan mai mutum biyar na kotun kolin karkashin jagorancin mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun ta yi watsi da karar jim kadan bayan masu daukaka karar sun janye karar.

A halin da ake ciki, kotun kolin ta dage ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Juma’a domin yanke hukunci kan sauran karar da Jibrin Barde na jam’iyyar PDP ya shigar.

Ganduje Ya Caccaki ‘Yan Siyasa Kan Lamarin Zaɓe a Najeriya

Kwamitin ya sanya ranar Juma’a ne domin yanke hukunci jim kadan bayan da bangarorin suka amince da kuma gabatar da jawaban da suka yi a cikin karar, wanda zai kare ranar Lahadi 21 ga watan Janairu.

Abba Gida-gida ya Fadi Rawar da Kwankwaso ya Taka a Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Kotun kolin ta fadawa lauyan ADC da lauyan Bala, Herbert Nwoye, cewa sun kasa kare wadanda suke tsayawa don haka sun kori karar, don gudun batawa kotun lokaci.

 

A wani labarin kuma Kotun kolin ta Jingine hukunci kan karar da Ashiru Isa na jam’iyyar PDP a jihar Kaduna ya shigar a kan zaben gwamna Uba Sani har zuwa ranar da za a sanar da dukkanin jam’iyyun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...