Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli Ta Yanke Hukuncin Kan Shari’ar Zaɓen Gwamnan Gombe

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Kotun koli ta yi watsi da karar da dan takarar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Nafiu Bala ya shigar kan zaben Muhammad Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan jihar Gombe.

Kwamitin alƙalan mai mutum biyar na kotun kolin karkashin jagorancin mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun ta yi watsi da karar jim kadan bayan masu daukaka karar sun janye karar.

A halin da ake ciki, kotun kolin ta dage ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Juma’a domin yanke hukunci kan sauran karar da Jibrin Barde na jam’iyyar PDP ya shigar.

Ganduje Ya Caccaki ‘Yan Siyasa Kan Lamarin Zaɓe a Najeriya

Kwamitin ya sanya ranar Juma’a ne domin yanke hukunci jim kadan bayan da bangarorin suka amince da kuma gabatar da jawaban da suka yi a cikin karar, wanda zai kare ranar Lahadi 21 ga watan Janairu.

Abba Gida-gida ya Fadi Rawar da Kwankwaso ya Taka a Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Kotun kolin ta fadawa lauyan ADC da lauyan Bala, Herbert Nwoye, cewa sun kasa kare wadanda suke tsayawa don haka sun kori karar, don gudun batawa kotun lokaci.

 

A wani labarin kuma Kotun kolin ta Jingine hukunci kan karar da Ashiru Isa na jam’iyyar PDP a jihar Kaduna ya shigar a kan zaben gwamna Uba Sani har zuwa ranar da za a sanar da dukkanin jam’iyyun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...