Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli Ta Yanke Hukuncin Kan Shari’ar Zaɓen Gwamnan Gombe

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Kotun koli ta yi watsi da karar da dan takarar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Nafiu Bala ya shigar kan zaben Muhammad Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan jihar Gombe.

Kwamitin alƙalan mai mutum biyar na kotun kolin karkashin jagorancin mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun ta yi watsi da karar jim kadan bayan masu daukaka karar sun janye karar.

A halin da ake ciki, kotun kolin ta dage ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Juma’a domin yanke hukunci kan sauran karar da Jibrin Barde na jam’iyyar PDP ya shigar.

Ganduje Ya Caccaki ‘Yan Siyasa Kan Lamarin Zaɓe a Najeriya

Kwamitin ya sanya ranar Juma’a ne domin yanke hukunci jim kadan bayan da bangarorin suka amince da kuma gabatar da jawaban da suka yi a cikin karar, wanda zai kare ranar Lahadi 21 ga watan Janairu.

Abba Gida-gida ya Fadi Rawar da Kwankwaso ya Taka a Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Kotun kolin ta fadawa lauyan ADC da lauyan Bala, Herbert Nwoye, cewa sun kasa kare wadanda suke tsayawa don haka sun kori karar, don gudun batawa kotun lokaci.

 

A wani labarin kuma Kotun kolin ta Jingine hukunci kan karar da Ashiru Isa na jam’iyyar PDP a jihar Kaduna ya shigar a kan zaben gwamna Uba Sani har zuwa ranar da za a sanar da dukkanin jam’iyyun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...