WHO ta gano sabon nau’in sauro da ke zagon-ƙasa ga yaƙi da Maleriya a wasu Kasashen Africa

Date:

 

Wani sabon nau’in sauro da ake yi wa lakabi da “steve,” wanda ya samo asali daga Kudancin Asiya, yana haifar da karuwar masu kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro a kasashen Afirka.

Kasashen African da sabon sauron yayi karuwa guda bakwai ne, da suka hada da Djibouti, da Habasha, da Kenya, da Najeriya, da kuma Ghana, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO).

Abba Gida-gida ya Fadi Rawar da Kwankwaso ya Taka a Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Ba kamar sauran sauro na yau da kullun ba, “steve” yana bunƙasa ne a cikin birane kuma ba ya bukatar danshi mai yawa kafin ya hayayyafa.

Ganduje Ya Caccaki ‘Yan Siyasa Kan Lamarin Zaɓe a Najeriya

Wannan nau’in sauron na cizo da rana, yana da juriya ga magungunan kashe ƙwari na yau da kullun, kuma yana haifar da ƙalubale ga dabarun yaƙi da zazzabin cizon sauro a halin yanzu, in ji Dr Dorothy Achu shugabar WHO kan cututtuka masu addabar mutanen da ke zaune a yankunan duniya masu zafi na Afirka, inda ta ƙara jaddada wahalar ganowa da kuma kawar da wannan sauro mai saurin jure yanayin.

BBC Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta nemi majalisar dokokin jihar ta haramta auren jinsi

Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci majalisar dokokin jihar ta...

Yan sanda a Kano sun lashi takobin samar da ingantaccen tsaro a ranar Takutaha

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori,...

Gwamnatin Kano Ta Ayyana Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gobe Juma’a, 12 ga...

INEC ta yi Allah-wadai da masu yakin neman zabe tun kafin lokaci ya yi

Hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta yi Allah wadai...