Ganduje Ya Caccaki ‘Yan Siyasa Kan Lamarin Zaɓe a Najeriya

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje yace ‘yan siyasa sune babbar matsalar Nigeria, musamman game da yadda ake gudanar da zabukan kasar.

Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Larabar da ta gabata yayin da ya karbi bakuncin daraktar zabe da sa ido na jam’iyyar na hukumar zabe ta kasa (INEC), Hawa Habibu.

Ya ce duk da cewa rashin tsaro babban abin damuwa ne wajen gudanar da zabe, amma ‘yan siyasa sun fi zama hadari.

Abba Gida-gida ya Fadi Rawar da Kwankwaso ya Taka a Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

“Na san daya daga cikin manyan matsalolin INEC wajen gudanar da zabe shi ne rashin tsaro. Mutane kuma na cewa INEC ce, amma ‘yan siyasa  suma matsala ce.

Kyautar Motar da aka Baiwa Jarumar Labarina Yasa Marubutan Kannywood Kokawa

“Don fahimtar ka’idoji da dokokin zabe akwai bukatar dan siyasa ya zama mai wayewa, cibiyoyinmu za su rika wayar da kan jama’armu lokaci zuwa lokaci ta yadda za su bi ka’idojin, kuma zai zama ta hanyar zamani .

“Mun kuma ba da umarnin cewa a dukkan ofisoshin jam’iyyarmu, tun daga mazabu zuwa kananan hukumomi, shiyyoyi da jihohi, dole ne a samu jami’ai.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...