Baza mu Saurarawa Duk Wanda ya Karya Doka Bayan Yanke Hukunci Zabe Gwamna Kano ba – Yan sanda

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

 

Mataimakin kwamishinan yan sanda mai kula da shiyar Bichi AC Yusif Dahiru Alkali ne ya bayyana cewa ba za su saurarawa duk wanda ya karya doka bayan kotun kolin Nigeria ta yanke hukuncin Shari’ar Zaɓen gwamnan jihar kano..

 

AC Yusuf Dahiru ya bayyana hakan ne yayi taro da Kungiyoyi da masu ruwa da tsaki na Kananan hukumomin dake Karkashin Shiyar Ofishin Yan sanda na Bichi.

AC Alkali yayi kira da iyaye dasu jawa ya’yan’su konne wajan bin doka da oda yayi sanar da hukunci zabe Gwamna da Kuma bayan hukunci zabe.

Talla

Mataimakin kwamishinan yace ana fakewa da murna daga karshe takoma fadace-fadace , don haka yace baza su lamunci hakan ba a gobe juma’a. Ya kuma tabbatar wa jama,a cewa kofar yan sanda abude take ba dare ba rana domin karbar rahotanni da zasu taimakawa rundunar.

Tarihin Alƙalin Da Zai Jagoranci Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Yakuma Shawarci iyaye dasu kara sanya idanu akan ya’yansu ya kuma ja hankalin yan siyasa da su guji dukkanin abinda zai kawo tada zaune tsaye a tsakanin Jama’a.

Anasa jawabin Shugaban kwamitin kyautata Alaka yan sanda da jama,ar Gari Mallam Garba Tukur, ya ce ashirye suke dasu bayar da dukkanin gudummawa domin Samar da cikar Tsaro a Shiryar ta Bichi

Ya kuma yi kira da yan siyasa dasu rugumi kaddara akan abinda zasuji na hukuncin da kotu Kolin.

Shari’ar Kano: Kotun Ƙoli ta Tsayar da Ranar Yanke Hukunci

Karshe Ya bukaci Shuwa gabannin dasuka zo sukoma suwayar wa jama,arsu kai akan zaman lafiya a tsakanin jama’a

Yayi taro Shuwagabanin kungiyoyin sunnuna jin dadinsu akan yadda Mataimakin kwamishinan ya karbesu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...