Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli ta Sanya Ranar Yanke Hukunci kan Shari’ar Zaɓen Gwamnan Zamfara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Kotun Kolin Nigeria ta ce ta sanya ranar Juma’a 12 ga Janairu, 2024 a matsayin ranar da zata yanke hukuncin kan shari’ar zaben gwamnan jihar Zamfara.

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da kotun kolin ta aikewa lauyoyin bangarorin biyu.

Talla

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Jam’iyyar APC da dan takarar ta na gwamnan jihar Bello Muhammad Matawalle ne suka daukaka kara zuwa kotun kolin don kalubalantar hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke.

Malam Shekarau Ya Yiwa Abba da Gawuna Nasiha Kan Hukunci Kotun Ƙoli

Ita dai kotun daukaka karar ta bukaci a sake zabuka a wasu mazabu dake jihar, lamarin da jam’iyyar APC tace bata lamunta ba hakan tasa ta garzaya kotun kolin.

Hukuncin kotun kolin dai shi ne zai kawo karshen ja’in jar da ake yi tsakanin jam’iyyar APC da PDP dake mulkin jihar karkashin gwamna Lawan Dare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...

Gwamnatin Kano Ta Kammala Aikin Gina Mayanka ta Naira Biliyan 1.5

Daga Zakaria Adam Jigirya     Gwamnatin jihar Kano ta karkashin Shirin...

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...