Tsadar Abinchi: Sanya Masu Sarautar Gargajiya a Harkokin Sayar da Takin Zamani ne zai Kawo Mafita – Alh. Abubakar Tabanni

Date:

Daga Shehu Husaini Getso

 

Wani fitaccen manomi a yankin karamar hukumar Gwarzo Alh Abubakar Usman Tabanni ya bukaci gwamnatocin tarayya da jihohi da su duba mawuyacin halin da al’ummar Nigeria suke ciki na tsadar kayayyakin abinci domin saukaka musu.

Alh Usman Tabanni yace tun ba’aje da nisa ba, a yanzu haka buhun masara a jihar Kano yana dosar zunzurutun kudi har Naira dubu Hamsin, wanda hakan yasa magidanta da dama basa iya ciyar da iyalinsu.

Alhaji Abubakar Tabanni
Alhaji Abubakar Tabanni

Alh. Abubakar Usman ya bayyana hakan ne lokacin da yake zanyawa da wakilin jaridar kadaura24 a Gwarzo, Kano.

Talla

Yace akwai tashin hankali kwarai da gaske ta yadda farashin kayayyakin abinci ke hauhawa kusan a kowacce rana a Nigeria.

“Hanya daya kawai da gwamnati zata iya shawo kan wannan matsala, ita ce kokarin wadata manoma da takin zamani a farashi mai rangwame, ta yadda manoma zasu sami saukin makudan kudaden da suke kashewa a harkokinsu na aikin gona”. Inji Alhaji Abubakar

Malam Shekarau Ya Yiwa Abba da Gawuna Nasiha Kan Hukunci Kotun Ƙoli

 

A cewarsa yana ganin don a sami nasarorin da ake bukata wajen tallafawa manoma, babu wata hanya da tallafin gwamnatoci zai dinga zuwa wajen manoma, fiye da tsarin shigo da masu sarautar gargajiya a cikin tsarin dari bisa dari, tunda su suka san manoma na hakika aduk inda suke.

Alh Abubakar Usman Tabanni ya yabawa Shugabanni da wakilan Yankin Kano ta Arewa a gwamnatin tarayya, bisa kokarin raya yankunan karkara,daga nan sai yayi kira ga masu ruwa da tsaki da su yi kokarin tabbatar da aikin titin daya tashi daga Getso ya shiga Zangon Mallam Gwani,dan-Nafada, yan-kwanci, katsalle da sauran garuruwan dake wannan rukuni domin saukakawa manoma ta fuskar harkokin sufuri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...