Malam Shekarau Ya Yiwa Abba da Gawuna Nasiha Kan Hukunci Kotun Ƙoli

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau ya yi kira da mabiya da shugabannin NNPP da na APC su rungumi hukuncin da kotun kolin ƙasar za ta yanke a matsayin ƙaddara.

Shekarau ya ce, ya yi imani da cewa babu wani zagi ko cin zarafi ko kuma kalaman ɓatanci da za su sauya hukuncin da kotu za ta yanke, ko kuma su sa a bai wa wani nasara a yayin hukuncin.

Talla

Shekarau ya yi wannan kira ne a wata tattaunawa da ya yi da gidan talabijin na Channels a wani shirin siyasa.

Da dumi-dumi: Kotun Koli ta Yanke Hukunci Kan Shari’ar Zaɓen Gwamnan Jihar Adamawa

Tun a watan Maris ɗin 2023 ne ake ta sa-toka-sa-katsi a kotu tsakanin Gwamna Abba Kabir Yusuf da kuma Nasiru Yusuf Gawuna kan kujerar gwamnan jihar Kano.

Shekarau ya ce “duk mutumin da ke bin siyasa ta, yasan siyasar zaman lafiya da kwanciyar hankali nake yi. Ina ɗaukar abokan siyasata abokaina ba tare da duba banbancin siyasa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...