Yanzu-yanzu: Betta Edu ta isa hedikwatar EFCC domin amsa tambayoyi

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Ministar ma’aikatar jin kai Dr. Betta Edu da aka dakatar a ranar Talata ta isa hedikwatar Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa zagon kasa (EFCC) bisa zargin almundahanar Naira miliyan 585 a ma’aikatar ta.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar Litinin ne shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Edu.

Talla

An zargi ministan da biyan kudaden jin kai a wani asusu na wata mata ta sirri.

Da dumi-dumi: Kotun koli ka iya yanke hukuncin shari’ar zaɓen Kano da Legas ranar Juma’a

An ce Naira miliyan 585 an yi amfani da shi ne don biyan tallafi ga marasa galihu a jihohin Akwa Ibom, Legas, Cross River da Ogun.

Edu dai ita ce minista ta farko da aka dakatar daga mukaminta, tun bayan rantsar da mambobin majalisar zartarwa ta shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a watan Agusta na bara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...