Yanzu-yanzu: Betta Edu ta isa hedikwatar EFCC domin amsa tambayoyi

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Ministar ma’aikatar jin kai Dr. Betta Edu da aka dakatar a ranar Talata ta isa hedikwatar Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa zagon kasa (EFCC) bisa zargin almundahanar Naira miliyan 585 a ma’aikatar ta.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar Litinin ne shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Edu.

Talla

An zargi ministan da biyan kudaden jin kai a wani asusu na wata mata ta sirri.

Da dumi-dumi: Kotun koli ka iya yanke hukuncin shari’ar zaɓen Kano da Legas ranar Juma’a

An ce Naira miliyan 585 an yi amfani da shi ne don biyan tallafi ga marasa galihu a jihohin Akwa Ibom, Legas, Cross River da Ogun.

Edu dai ita ce minista ta farko da aka dakatar daga mukaminta, tun bayan rantsar da mambobin majalisar zartarwa ta shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a watan Agusta na bara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...