Juyin Mulkin Nijar: Sakin Matar Bazoum Da Dansa, Zai Taimaka Kan Dage Takunkumin ECOWAS– Ministan Kasashen Waje

Date:

Daga Halima Musa Abubakar

 

Ministan Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa, sakin matar Mohammed Bazoum da dansa da sojojin juyin Mulki suka yi a Nijar wani mataki ne mai ma’ana na maido da zaman lafiya a kasar da ma yankin baki daya.

Tuggar, wanda kuma ke rike da mukamin shugaban kwamitin sulhu da tsaro, ya yabawa majalisar tsaro ta kasar da ta sake su daga kullen gida tun bayan hambarar da gwamnatin Muhammadu Bazoum.

Da dumi-dumi: Kotun koli ka iya yanke hukuncin shari’ar zaɓen Kano da Legas ranar Juma’a

Ya kuma sake yin kira ga gwamnatin karkashin jagorancin Janar Abdourahamane Tchiani da ta gaggauta sakin Mohammed Bazoum daga hannun ta.

Tuggar ya bukace su da su kyale Bazoum ya fita zuwa wata kasa, inda ya ce, hakan, zai zama wani muhimmin mataki na samar da damar ci gaba da tattaunawa kan dage takunkumi da aka kakaba wa kasar. Ya kara da cewa, hakan na da matukar muhimmanci ga samun walwala da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Nijar da ma yankin baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...