Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli ta Yanke Hukunci kan Shari’ar zaɓen gwamnan jihar Benue

Date:

Kotun ƙoli ta yi fatali da ƙarar da aka ɗaukaka kan zaɓen gwamna Hycinth Alia na jihar Benue.

Matakin na zuwa ne bayan janye ƙarar da lauyan Mr Titus Uba na Jam’iyyar PDP, Sebastian Hon ya yi.

Titus Uba ya ƙalubalanci nasarar gwamna Hyacinth ne na jam’iyyar APC.

Talla

Sai dai kotun ƙararrakin zabe da ta ɗaukaka ƙara a Abuja sun tabbatar Alia ne halastaccen gwamnan jihar ta Benue bayan da hukumar aɓe INEC ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen ranar 18 ga watan Maris.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta ce ba ta da hurumin sauraron ƙarar da aka shigar gabanta saboda batutuwan da aka yi ƙorafi a kansu sun faru ne gabanin zaɓen.

Da dumi-dumi: Kotun koli ka iya yanke hukuncin shari’ar zaɓen Kano da Legas ranar Juma’a

Kotun ta kuma ce kamata ya yi Uba ya maka mataimakin gwamna Sam Ode a babbar kotu bisa zargin mallakar takardar boge.

Ta kuma ce Uba ya gaza tabbatar da zarge-zargen da yake yi wa mataimakin gwamnan.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa yau litinin ne kotun zata yanke hukuncin karshen kan shari’ar zaɓen gwamnan jihar Benue da ta wasu jihohi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...